Far 17:20-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Ga zancen Isma'ilu kuwa, na ji, ga shi, zan sa masa albarka in kuma riɓaɓɓanya shi ainun. Zai zama mahaifin 'ya'yan sarakuna goma sha biyu, zan maishe shi al'umma mai girma.

21. Amma ga Ishaku ne zan tsai da alkawarina, wato wanda Saratu za ta haifa maka a baɗi war haka.”

22. Sa'ad da Allah ya gama magana da Ibrahim, sai ya tafi ya bar Ibrahim.

23. Ibrahim kuwa ya ɗauki Isma'ilu ɗansa, da dukan bayi, haifaffun gidansa, da waɗanda aka sayo su da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji na jama'ar gidansa kaciyar loɓarsa a wannan rana bisa ga faɗar Allah.

24. Ibrahim na da shekara tasa'in da tara sa'ad da aka yi masa kaciyar loɓarsa.

25. Isma'ilu ɗansa yana ɗan shekara goma sha uku sa'ad da aka yi masa kaciya.

26. A wannan rana, Ibrahim da ɗansa Isma'ilu aka yi musu kaciya,

Far 17