1. A lokacin da Abram yake da shekara tasa'in da tara Ubangiji ya bayyana gare shi, ya ce masa, “Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka yi mini biyayya, ka zama kamili.
2. Zan yi maka alkawari, in ba ka zuriya mai yawa.”
3. Sai Abram ya yi ruku'u, Allah kuwa ya ce masa,