1. Domin haka Abram ya bar Masar zuwa Negeb, shi da matarsa, da abin da yake da shi duka tare da Lutu.
2. Yanzu Abram ya arzuta da dabbobi, da azurfa, da zinariya.
3. Ya yi ta tafiya daga Negeb har zuwa Betel, har wurin da ya kafa alfarwarsa da fari, tsakanin Betel da Ai,
4. a inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
5. Lutu wanda ya tafi tare da Abram, shi kuma yana da garkunan tumaki, da na shanu, da alfarwai,