3. Allah ya ce, “Bari haske ya kasance,” sai kuwa ya kasance.
4. Allah ya ga hasken yana da kyau. Allah ya raba tsakanin hasken da duhu,
5. ya ce da hasken, “Yini,” duhu kuwa, “Dare.” Ga maraice, ga safiya, kwana ɗaya ke nan.
6. Allah ya ce, “Bari sarari ya kasance tsakanin ruwaye, don ya raba tsakaninsu.”
7. Allah kuwa ya yi sarari, ya kuma raba tsakanin ruwayen da suke ƙarƙashin sararin da ruwayen da suke birbishin sararin. Haka nan kuwa ya kasance.