Ez 47:21-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. “Za ku kuwa raba ƙasar a tsakaninku bisa ga kabilan Isra'ila.

22. Za ku raba ƙasar gādo a tsakaninku da baƙin da suke zaune tare da ku, waɗanda suka haifi 'ya'ya a cikinku. Za su zama kamar 'ya'yan Isra'ila haifaffu na gida. Za a ba su gādo tare da kabilan Isra'ila,

23. a cikin kabilar da baƙon yake zaune, nan ne za ku ba shi nasa gādo, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ez 47