Ez 46:20-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Sai ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya domin laifi, da hadaya domin zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gāri, domin kada su kai su a filin waje, su sa wa mutane tsarki.”

21. Ya kuma kai ni a farfajiyar waje, ya bi da ni zuwa kusurwa huɗu na farfajiya. Akwai ɗan fili a kowace kusurwa.

22. Girman kowane ɗan fili tsawonsa kamu arba'in ne, faɗin kuma kamu talatin.

Ez 46