Ez 30:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce,

2. “Ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce Ubangiji Allah ya ce maka ka yi kuka, kana cewa,‘Kaito, kaito saboda wannan rana!’

3. Gama ranar ta gabato,Ranar Ubangiji ta yi kusa,Rana ce ta gizagizai,Ranar halakar al'ummai.

4. Takobi zai fāɗa a kan Masar,Azaba kuma za ta sami Habasha.Za a kashe mutane a Masar,Za a kwashe dukiyarta,A rushe harsashin gininta.

5. “Yaƙi zai ci Habasha, da Fut, da Lud, da dukan Arabiya, da Libya, da mutanen ƙasar da suka haɗa kai da su.”

Ez 30