Ez 19:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Sai ka yi makoki domin hakiman Isra'ila,

2. Ka ce, ‘Mahaifiyarka zakanya ce a cikin zakoki,Ta yi zamanta tare da 'yan zakoki,Ta yi renon kwiyakwiyanta.

3. Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta,Ya zama sagari,Sai ya koyi kamun nama, ya cinye mutane.

4. Da al'ummai suka ji labarinsa,Sai suka kama shi cikin wushefensu,Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa Masar.

Ez 19