1. “Sai ka yi makoki domin hakiman Isra'ila,
2. Ka ce, ‘Mahaifiyarka zakanya ce a cikin zakoki,Ta yi zamanta tare da 'yan zakoki,Ta yi renon kwiyakwiyanta.
3. Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta,Ya zama sagari,Sai ya koyi kamun nama, ya cinye mutane.