22. Ga abin da Ubangiji Allah ya ce,“Ni kaina zan cire toho a kan itacen al'ul mai tsawo.Daga cikin sababbin rassansa zan karya lingaɓu,In dasa shi a tsauni mai tsayi.
23. A ƙwanƙolin tsaunin Isra'ila zan dasa shiDon ya fito da rassa, ya ba da 'ya'ya,Ya zama itacen al'ul na gaske.Tsuntsaye iri iri za su zauna a ƙarƙashinsa,Za su yi sheƙuna a cikin inuwar rassansa.
24. Dukan itatuwan jeji za su sani,Ni Ubangiji nakan sa manyan itatuwa su zama ƙanana,In sa ƙanana kuma su zama manya,In sa ɗanyen itace ya bushe,In sa busasshen itace kuma ya zama ɗanye, Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.”