Dan 4:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Wannan shi ne hukuncin da tsarkaka,Masu tsaro suka shawarta,Suka yanke domin masu rai su saniMaɗaukaki yake sarautar 'yan adam,Yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama,Yakan sa talaka ya zama sarki.”

18. “ ‘Mafarkin da ni sarki Nebukadnezzar na yi ke nan. Kai Belteshazzar kuma, sai ka faɗa mini ma'anarsa, domin dukan masu hikima na cikin mulkina ba su iya faɗar mini ma'anar, amma kai ka iya, gama ruhun alloli tsarkaka yana cikinka.’ ”

19. Daniyel kuwa wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar, ya tsaya zugum da ɗan daɗewa, tunaninsa ya ba shi tsoro. Sarki ya ce, “Belteshazzar, kada ka bar mafarkin ko ma'anarsa ya ba ka tsoro.”Sai Belteshazzar ya amsa, ya ce, “Ya shugabana, Allah ya sa mafarkin nan, da ma'anarsa, su zama a kan maƙiyanka.

20. Itacen nan da ka gani wanda ya yi girma, ya ƙasaita, ƙwanƙolinsa ya kai sama, har ana iya ganinsa daga ko'ina a duniya,

Dan 4