12. “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi?Kana tsammani ni dodon ruwa ne?
13. Na kwanta ina ƙoƙari in huta,Ina neman taimako don azabar da nake sha.
14. Amma kai kana firgita ni da mafarkai,Kana aiko mini da wahayi da ganegane,
15. Har nakan fi so a rataye ni,Gara in mutu da in rayu a wannan hali.
16. Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa.Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana.