1. Ayuba ya amsa.
2. “In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma'auni,
3. Da sun fi yashin teku nauyi.Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi.
4. Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau,Dafinsu kuwa ya ratsa jikina.Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.
5. “Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya,In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne.
16-17. Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara,Amma lokacin zafi sai su ɓace,Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.