7. Idan dai na kauce daga hanya,Ko kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna,Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna,
8. To, bari in shuka, wani ya ci amfanin,Bari a tumɓuke amfanin gonata.
9. “Idan na yi sha'awar wata mace,Har na je na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10. To, bari matata ta yi wa wani abinci,Bari waɗansu su kwana da ita.
11. Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai,Wanda alƙalai ne za su hukunta.