30. Ban yi zunubi da bakina ba,Ban nemi ran wani ta wurin la'anta shi ba.
31. Ko mutanen da suke cikin alfarwata ba wanda zai ce,Ga wani can da bai ƙoshi da nama ba.
32. Ban bar baƙi su kwana a titi ba,Ƙofar gidana a buɗe take ga matafiya.
33. Idan na ɓoye laifofina a zuciyata,
34. Ko na tsaya shiru saboda tsoron taron jama'a,Saboda kuma baƙar maganar mutane ta razanar da ni,
35. Da a ce ina da wanda zai kasa kunne gare ni,Da sai in sa hannu a kan abin da na faɗa,Allah kuwa Mai Iko Dukka ya amsa mini.“Da ƙarar da maƙiyana suke kai ni, a rubuce ne,