4. Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci,Sukan ci doyar jeji.
5. Aka kore su daga cikin mutane,Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo,
6. Sai a kwazazzabai suke zamaDa a ramummuka da kogwannin duwatsu.
7. Suka yi ta kuka a jeji,Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya.
8. Mutane ne marasa hankali marasa suna!Aka kore su daga ƙasar.
9. “Yanzu na zama abin waƙa gare su,Abin ba'a kuma a gare su.
10. Suna ƙyamata, guduna suke yi,Da ganina, sai su tofa mini yau.
11. Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni,Saboda haka sun raba ni da zuriyata,
12. A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini,Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa.
13. Sun datse hanyata,Sun jawo mini bala'i,Ba kuwa wanda ya hana su.
14. Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka,Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi.
15. Sun firgita ni,Sun kori darajata kamar da iska,Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije.
16. “Yanzu zuciyata ta narkeKwanakin wahala sun same ni.
17. Da dare ƙasusuwana karkaɗuwa suke,Azaba tana ta gaigayata ba hutawa.
18. An yi mini kamun kama-karya,An ci wuyan rigata.
19. Allah ya jefar da ni cikin laka,Na zama kamar ƙura ko toka,
20. “Na yi kira gare ka, ya Allah, amma ba ka amsa mini ba,Na yi addu'a kuma, amma ba ka kula da ni ba.
21. Ka zama mugu a gare ni,Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.
22. Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta,Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri.
23. Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa,Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai.