21. Ka zama mugu a gare ni,Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.
22. Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta,Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri.
23. Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa,Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai.
24. “Ashe, wanda yake gab da gagarumar hallaka,Ba zai miƙa hannu ya roƙi taimako a masifar da yake sha ba?
25. Ashe, ban yi kuka saboda wanda yake shan wahala ba?Ashe, ban yi ɓacin rai saboda matalauta ba?