1. “Amma yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a suke mini,Waɗanda iyayensu maza ba su fi karnukan da suke kiwon garken tumakina ba.
2. Wace riba zan samu ta wurin ƙarfin hannuwansu waɗanda ba su da sauran kuzari?
3. Saboda rashi da matsananciyar yunwa sun rame,Sai gaigayar ƙasa suke yi da dare, a cikin kufai.