8. Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah?Sa'ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa?
9. Allah kuwa zai ji kukansa sa'ad da wahala ta same shi?
10. Ko Mai Iko Dukka zai zama abin farin ciki a gare shi?Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11. “Zan koya muku zancen ikon Allah,Abin da yake na wajen Mai Iko Dukka ba zan ɓoye ba.
12. Ga shi kuwa, dukanku kun gani da kanku,Me ya sa kuka zama wawaye?