Ayu 27:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ayuba ya amsa.

2. “Na rantse da Allah Mai Iko Dukka,Wanda ya ƙwace mini halaliyata,Wanda ya ɓata mini rai.

3. Muddin ina numfashi,Ruhun Allah kuma yana cikin hancina

4. Bakina ba zai faɗi ƙarya ba,Harshena kuma ba zai hurta maganganun yaudara ba.

5. Allah ya sawwaƙa in ce kun yi daidai,Har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba.

Ayu 27