Ayu 23:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ayuba ya amsa.

2. “Duk da haka zan yi tawaye in yi wa Allah gunaguni,In dinga yin nishi.

3. Da ma na san inda zan same shi,In kuma san yadda zan kai wurinsa,

4. Da zan kai ƙarata a gare shi, in faɗa masa duk muhawarata, in kāre kaina ne.

5. Ina so in san irin amsar da zai mayar mini,Ina kuma so in san yadda zai amsa mini.

Ayu 23