10. Don haka ne yanzu akwai ramummuka ko'ina kewaye da kai,Tsoro ya kama ka nan da nan.
11. An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani,Rigyawa ta sha kanka.
12. “Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba?Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne.
13. Duk da haka ka ce, ‘Allah bai san kome ba.Gizagizai sun lulluɓe shi, ƙaƙa zai iya yi mana shari'a?’