6. Sa'ad da na tuna da abin da ya same ni,Sai jikina ya yi suwu, in yi ta makyarkyata ina rawar jiki.
7. Me ya sa Allah yake barin mugayeHar su tsufa su kuma yi arziki?
8. 'Ya'yansu da jikokinsu sukan girma a idonsu.
9. Allah bai taɓa aukar wa gidajensu da bala'i ba,Ba su taɓa zama a razane ba.
10. Hakika shanunsu suna ta hayayyafa,Suna haihuwa ba wahala.
11. 'Ya'yansu suna guje-guje,Suna tsalle kamar 'yan raguna,
12. Suna rawa ana kaɗa garaya,Ana busa sarewa.
13. Suka yi zamansu da salama,Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba.
14. Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum,Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.
15. Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah,Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida.