1. Ayuba ya amsa.
2. “Ku kasa kunne ga abin da nake faɗa,Wannan ita ce ta'aziyyar da nake nema a gare ku.
3. Ku ba ni zarafi in yi magana, sa'an nan in na gama ku amsa in kun ga dama.
4. “Ba da 'yan adam nake faɗa ba,Ina da isasshen hanzarin da zai sa in yi fushi.