7. Me ya sa kuke yin ƙarya?Kuna tsammani ƙarairayinku za su taimaki Allah?
8. Son zuciya kuke yi, ko ba haka ba?Kuna goyon bayan Allah?Za ku goyi bayan Allah sa'ad da aka gurfanar da ni gaban shari'a?
9. Da Allah ya bincike ku sosai,Zai iske wani abin kirki ne a cikinku?Kuna tsammani za ku ruɗi Allah, kamar yadda kuke ruɗin mutane?
10. Ko da yake kun ɓoye son zuciyarku,Duk da haka zai tsauta muku,
11. Ikonsa kuwa zai razana ku.
12. Karin maganarku da muhawararku ba su da ƙarfi ƙwarai.