A.m. 8:13-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Har Saminu da kansa ma ya ba da gaskiya, bayan an yi masa baftisma kuma ya manne wa Filibus. Ganin kuma ana yin mu'ujizai da manyan al'ajibai, ya yi mamaki ƙwarai.

14. To, da manzannin da suke Urushalima suka ji Samariyawa sun yi na'am da Maganar Allah, suka aika musu da Bitrus da Yahaya.

15. Su kuwa da suka iso, suka yi musu addu'a don su sami Ruhu Mai Tsarki,

16. domin bai sauko wa ko wannensu ba tukuna, sai dai kawai an yi musu baftisma ne da sunan Ubangiji Yesu.

17. Sai suka ɗora musu hannu, suka kuwa sami Ruhu Mai Tsarki.

A.m. 8