3. kullum muna yarda da haka ƙwarai a ko'ina, tare da godiya ba iyaka.
4. Amma don kada in gajiyad da kai, ina roƙonka a cikin nasiharka, ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5. Mun tarar da mutumin nan fitinanne ne, yana ta da hargitsi tsakanin Yahudawa ko'ina a duniya, shi kuma ne turun ɗariƙar Nazarawa.
6. Har ma yana nema ya tozarta Haikali, amma muka kama shi. [Niyyarmu ce mu hukunta shi bisa ga shari'armu.
7. Amma shugaba Lisiyas ya zo ya ƙwace shi daga hannunmu ƙarfi da yaji,
8. ya yi umarni masu ƙararsa su zo a gabanka.] In kuwa ka tuhume shi da kanka, za ka iya tabbatarwa daga bakinsa duk ƙarar da muke tāsarwa.”
9. Yahudawa ma suka goyi bayan haka, suna tabbatarwa haka abin yake.