13. ya zo ya tsaya a kusa da ni, ya ce mini, ‘Ya ɗan'uwana Shawulu, ganinka yă komo maka.’ Nan tāke, sai ganina ya komo, na kuwa gan shi.
14. Sai ya ce, ‘Allahn kakanninmu ya zaɓe ka don kă san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji jawabi daga bakinsa.
15. Don za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane game da abin da ka gani, ka kuma ji.
16. To, a yanzu me kake jira? Tashi, a yi maka baftisma a wanke zunubanka ta wurin kira bisa sunansa.’ ”
17. “Da na komo Urushalima, ina addu'a a Haikali, sai wahayi ya zo mini.