32. Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka.
33. Da yake an ɗaukaka shi a dama ga Allah, ya kuma sami cikar alkawarin nan na baiwar Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, sai ya zubo da wannan da kuke gani, kuke kuma ji.
34. Ai, ba Dawuda ne ya hau Sama ba, amma shi kansa ya ce,‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,Zauna a damana,
35. Sai na sa ka take maƙiyanka.’
36. “Don haka sai duk jama'ar Isra'ila su sakankance, cewa shi Yesun na da kuka gicciye, Allah ya mai da shi Ubangiji, da kuma Almasihu.”
37. To, da suka ji haka, maganar ta soke su a zuci, suka ce wa Bitrus da sauran manzannin, “'Yan'uwa, me za mu yi?”