31. Su kuwa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
32. Sa'an nan suka gaya masa Maganar Ubangiji, shi da iyalinsa duka.
33. Nan take da daddaren nan ya ɗebe su, ya wanke musu raunukansu. Nan da nan kuwa aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
34. Sa'an nan ya kawo su gidansa, ya kawo musu abinci, ya yi ta farin ciki matuƙa, domin shi da iyalinsa duka sun gaskata da Allah.
35. Amma da gari ya waye, sai alƙalan suka aiko dogarai, suka ce, “Suka ce a saki mutanen nan.”
36. Yari kuwa ya shaida wa Bulus maganar, ya ce, “Alƙalai sun aiko a sake ku, saboda haka yanzu sai ku fito, ku tafi lafiya.”