16. Da an yi wannan sau uku, nan da nan aka yi sama da abin.
17. Bitrus na a cikin damuwa ƙwarai a kan ko mece ce ma'anar wahayin da aka yi masa, sai ga mutanen da Karniliyas ya aiko tsaye a ƙofar zaure, sun riga sun tambayi gidan Saminu,
18. suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka.
19. Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka.