1. A ƙarshen shekara ashirin waɗanda Sulemanu ya yi yana gina Haikalin Ubangiji da fādarsa,
2. sa'an nan ya sāke giggina biranen da Hiram ya ba shi, ya zaunar da Isra'ilawa a cikinsu.
3. Sai Sulemanu ya tafi ya ci Hamat-zoba da yaƙi.
4. Sa'an nan ya gina Tadmor a jeji, a Hamat kuwa ya gina biranen ajiya.