2 Tar 8:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A ƙarshen shekara ashirin waɗanda Sulemanu ya yi yana gina Haikalin Ubangiji da fādarsa,

2. sa'an nan ya sāke giggina biranen da Hiram ya ba shi, ya zaunar da Isra'ilawa a cikinsu.

3. Sai Sulemanu ya tafi ya ci Hamat-zoba da yaƙi.

4. Sa'an nan ya gina Tadmor a jeji, a Hamat kuwa ya gina biranen ajiya.

2 Tar 8