2 Kor 6:16-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Wace yarjejeniya ce take a tsakanin Haikalin Allah da gumaka? Domin mu haikali ne na Allah Rayayye. Yadda Allah ya ce,“Zan zauna tare da su, in yi yawo a tsakaninsu,Zan kuma kasance Allahnsu,Su kuma su kasance jama'ata.

17. Saboda haka, sai ku fito daga cikinsu,Ku keɓe, in ji Ubangiji,Kada ku ko taɓa wani abu marar tsarki,Ni kuwa in yi na'am da ku,

18. In kasance Uba a gare ku,Ku kuma ku kasance 'ya'yana, maza da mata,In ji Ubangiji Maɗaukaki.”

2 Kor 6