15. Fahariyarmu ba fiye da yadda ya kamata take ba, ba ta kuma shafi aikin waɗansu ba. Amma muna sa zuciya bangaskiyarku ta riƙa ƙaruwa, ta haka kuma fagen aikinmu a cikinku ya riƙa ƙaruwa ƙwarai da gaske,
16. har ma mu samu mu yi bishara a ƙasashen da suke a gaba da ku, ba tare da wata fahariya da aikin da wani ya riga ya yi a fagensa ba.
17. Amma, “Duk mai yin fahariya, ya yi fahariya da Ubangiji.”
18. Ai, ba mai yabon kansa ake yarda da shi ba, sai dai wanda Ubangiji ya yaba wa.