1 Tim 2:12-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Ban yarda mace ta koyar, ko kuma ta yi iko da maza ba, sai dai ta zama shiru.

13. Ai, Adamu aka fara halitta, sa'an nan Hawwa'u.

14. Ba kuma Adamu aka yaudara ba, amma matar ce aka yaudara, har ta keta umarni.

15. Duk da haka kuwa, ta wurin haifar 'ya'ya sai ta kai ga kammala, muddin ta nace wa bangaskiya, da ƙauna, da zama a tsarkake, da kuma kamunkai.

1 Tim 2