1 Tas 5:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Kada ku danne maganar Ruhu.

20. Kada ku raina annabci,

21. sai dai ku jarraba kome, ku riƙi abin da yake nagari kankan.

22. Ku yi nesa da kowace irin mugunta.

23. Allah kansa, mai zartar da salama, yă tsarkake ku sarai, ya kuma kiyaye ruhunku da ranku da jikinku ƙalau, ku kasance marasa abin zargi a ranar komowar Ubangijinmu Yesu Almasihu.

1 Tas 5