1. Dawuda ya yi tunani a ransa, ya ce, “Wata rana Saul zai kashi ni, don haka ba abin da ya fi mini, sai in tsere zuwa ƙasar Filistiyawa. Sa'an nan Saul zai fid da zuciya ga nemana a ƙasar Isra'ila. Zan kuwa tsira daga hannunsa.”
2. Dawuda ya tashi tare da mutum ɗari shida da suke tare da shi zuwa wurin Akish, ɗan Mawok, Sarkin Gat.